
Cikakken rahoton ziyarar zumunci da aka gudanar a garin Zariya, ciki har da ganawa da iyalan shahidai, dattawan gari da malaman addini.

An gudanar da muhimman ziyarce-ziyarce na zumunci da sadar da zumunta a sassan tsohon birnin Zariya da ke jihar Kaduna, inda aka gana da jama'a, dattawa, da iyalan shahidai.
Babban abin da ziyarar ta fi mayar da hankali a kai shi ne shiga gidajen iyalan shahidan da suka sadaukar da rayukansu a lokutan hare-haren da suka gabata a Zariya, tare da karfafa musu gwiwa da addu'ar daukaka.
"Juriyarku da hakurinku abin koyi ne ga daukacin al'umma, kuma sadaukarwar da kuka yi za ta ci gaba da zama abin alfahari a tarihin neman adalci."
An kuma yi zama na musamman tare da malaman addini da dattawan unguwanni domin tattauna hanyoyin inganta jin dadin al'umma, zaman lafiya da taimakon marasa galihu a jihar Kaduna.